Kalaman Soyayya Ga Budurwa

 

  1. Dafatan kina lafiya masoyiya? Na kasa samun natsuwa a cikin zuciya ta. Kunnuwa na muryar ki kawai take muradin ji, Idanuna fuskar ki take muradin gani, tinanin ki ke sani farin ciki a koda yaushe. Ina kaunar ki.

  2. Na dade ina neman hanyar da yace na fada maki sakon da zuciya ta ta aiko ni, amma kwarjinin ki yasa na kasa tinkarar ki, hakan na neman ya haifar mun matsala, samun ki a rayuwata itace babban muradi na. tun daga ranar da na fara saki a idanuna, na fara ji a zuciyata na samu babbar rabo.

  3. Masoyiya ta, inaso kiyi mun wata alfarma. Inaso muryar ki tazamo muryar da zan fara ji duk safiya inna tashi, kuma tazamo muryar da zan ji kafin in kwanta. Zan iya samun wannan alfarmar kuwa?

  4. Ina mai matukar godiya da farin ciki a dalilin samun ki a rayuwa ta. Na daina shiga bakin ciki da damuwa tunda nayi nasarar samun ki. Ina son ki bilhaqqi har cikin zuciya ta.

  5. Kyawun ki, ilimin ki da kuma far’ar ki shiyasa nakamu da son ki, duk abunda zai bata maki rai, ko yasa ki shiga damuwa, na daina wannan abun har abada.

  6. Baki san wani abu ba. Duk sanda na kalli fuskar ki yayin da kike murmushi, ko na kalli kafafuwan ki idan kina tafiya, sai na ji dadin da ba tabajin irin sa. Kasan cewar ki a rayuwa ta, silar farin ciki ne da nishadi mai dorewa.

  7. Dafatan kintashi lafiya, bayan na tashi bacci, sai nakejin damuwa a zuciya ta bansan silar hakan ba, sai nafara tambayan zuciya ta menene banyi ba. Nan take sai na samu maganin hakan. Jin muryar ki a duk safiya, kawai ta ishe ni farin ciki na tsawon wuni guda.

  8. Duk inna zo zance wurin ki, sai naji kamar kar na tashi, kunnuwa na basu gajiya da jin muryar ki, zuciya ta bata iya jurar rashin ki a cikin ta. Zuciya ta tana kewar ki.

  9. Soyayyar ki tasa na fara ji na kamar sarki ba tare da sarauta ba, shugaba batare da mutane ba, malami ba tare da dalibai ba, commander ba tare da sojoji ba, jarimi ba tare da mayaka ba, farin cikin kawai ta ishe ni komai a duniya.

  10. Har ila rana irin ta yau, abokaina na kishi a kanki, dan farin cikin da nake samu a wurin ki, bata iya misaltuwa da wacce suke samu a wurin budurwar su, kuma hakan sawa yake kaunarki ta kara yawa a cikin zuciyata.

  11. Akan ce ko wata mace nada kyau. Amma bantaba sanin me kalmar kyau ke nufi ba sai nayi nasarar samunki a rayuwa ta, kuma zanyi iya bakin kokari na naga na faranta maki rai.

  12. Sarauniya ta, a duk sanda kike cikin damuwa ko bacin rai, ina mai neman alfarmar ki, ki sanar da ni, soboda shigar ki cikin damuwa, bakin ciki ne da bacin rai a zuciya ta.

  13. Duk inna zauna a gida ina tinanin ki, sai na fara murmushi, aita tambaya ta meke damunka, amsa ta itace samun sarauniya irin ki a rayuwa ta.

  14. Har kishi nake naji wani ya amba ci  sunan ki, amma asanda na duba naga ba ke bace, sai naji dadi, dan bazan iya jurar ganin ki da wani namiji ba.

  15. Wasu lokutan sai naji kamar kasancewar ki a rauyawa ta kamar mafarki ne, gaskiya ina kara godewa ubangiji daya hada mu tare.

  16. Duk in zan rubuta sunana a littafi, alkalamin rubutu na sai yaki rubutun, sai nayi tinanin na rubuta sunan ki tukunna, sau daya ina gwadawa sai ga sunan ki a rubuce, alkalamin rubutu na ya shaida da kyawun ki da fasahar ki.

  17. Nifa tunda nafara kallan fuskar ki zuciya ta ta tabbatar mun da na sami abokiyar farin ciki wacce zata zamo silar farin ciki da walwala a zuciya ta. Kuma zanyi duk abunda zai sa hakan ta tabbata.

  18. A duk ranar duniya, sai soyayyar ki ta koya mun wani darasi na rayuwa wanda a gurin ki kawai ne zan iya samun hakan. Kuma zanyi iya bakin kokari na nayi amfani da wannan darasi gwargwadon iko.

  19. Inaso kisaka a ranki, duk abunda ya faru da ke walau farin ciki ko bakin ci, ina tare da ke dari bisa dari.

  20. Zuciyar ki cike take da kauna, kinzamo irin budurwar da duk da namiji ke muradin samu a duniyar nan. Nidai ina mai farin cikin samun ki a rayuwa ta.

  21. Kafin samun ki a rayuwa, nazamo mai yawan tinani, ban jindadin komai kuma ban iya gayawa kowa damuwa ta, amma tunda nayi nasarar samun ki a zuciya ta, komai sai yazo mun da sauki, naji dadi sosai kam.

  22. Kalamai ko aikatau bazasu taba iya misalta irin son da nake maki ba, ubangiji ma hallici yasa wannan soyayyar tamu mai dorewa ce kuma yasa mu cinma burin mu na rayuwa.

  23. A rayuwa ta ni kam nasamu rabo, samun budurwa irin ki kawai kawai ta ishe ni komai a duniyar nan don nishadin dake cikin soyayya dake itace abin nema.

  24. Ban taba sanin haka so ke da kyawu ba sai da nayi nasarar samun ki a zuciya ta. Irin son da nake maki bazai misaltu ba.

  25. Matukar ina duniya kuma akwai rai a jikina, babu abunda zai iya ja da soyayyar ki a zuciya ta.

  26. Kasancewar ki a rayuwa ta kara haskaka zuciya ta alokacin da banta ba tsammani ba. Bakin ciki ta koma farin ciki, damuwa ta koma nishadi, kuma hakan ta isheni arziki.

  27. A baya nashiga wasu hali marasa dadi kafin samun ki, amma yanzu duk soyayyar ki tasa na manta dasu.

  28. Ji nake kamar nazo na tare a gidan ku dan nagaji da kewar ki. Zuciya ta ta kasa samun sukuni, fuskar ki take muradin gani.

  29. Koda ace zan manta wani abu a rayuwa ta, bazan taba manta ran da nafara ganin ki ba. Wannan ranan yazama cikin kyakkwawar tarihin rayuwa ta.

  30. Sakon soyayya daya tak daga gare ki ta ishe ni farin ciki awuni daya.

  31. Daga lokacin da muka fara haduwa har zuwa yau, farin ciki da nishadi itace abun da nake fuskanta daga gare ki, gaskiya nayi sa’a sosai.

  32. A kullin, shagaltuwa nake da tinanin irin kyawun ki, in da ace zaki iya kallon kanki kamar yadda ake kallon ki, da zaki gane cewa a cikin masu kyau, ke ta daban ce, kuma na rabauta da samun ki a rayuwa ta.

  33. Inda ace akwai wata sabuwar hanyar da zan iya nuna maki irin kaunar danake maki, da nayi hakan cikin farin ciki amma duk da hakan bazan manta irin farin cikin da nasamu soboda ke ba.

  34. Inda ace zama saurayin ki aiki ne, ina mai yi maki alkawarin cewa duk shekara ni za’a bama kyautar karramawa dan bazanyi kasa a gwiwa wajen ganin na faranta maki ba.

  35. Aduk lokacin da ake gayamun wani abu da kikayi a baya, sai naji na kara sonki fiye da yadda nake yi gabanin hakan.

  36. Ana yawan cewa kyawun mace na iya juya tinanin samarai, nine a gaba wajen karyata hakan, amma yau na dauki darasi babba, dan inna kalli fuskar ki manta kaina nake. Jinake kamar inta kallon fuskar ki har abada.

  37. Taya nake iya gane irin son da nake maki? A duk sanda waya ta ta buga, tinanin ki ke fara shiga zuciya ta, har wani bakin ciki nake ji a sanda na dauka ba ke bace, amma kuma in ke ce, har kosawa nake in dauka.

  38. Kowa a duniyar nan nada abunda inya tina yake kara mai kwarin gwiwa da kwazo a hidimar sa, masoyiya ta abar kauna ta, kinzamo dalilin duk wata nasarar da nake samu.

  39. Ganin murmushin ki mai kayatarwa da sa annashuwa kadai ya ishe ni farin ciki, farin cikin ki ce muradin zuciya ta a kullin.

  40. Kafin nasan me so, ina ganin duk wani mai soyayya bai da aikin yi, amma bayan sanin ki, nayi nadama akan hakan dan kuwa ban san irin farin cikin da suke samu ba. Amma yanzu kam nasani.

  41. Masoyiya ta abar kauna ta, zan iya baki duk abun da kike so acikin duniyar nan matukar bai fi karfina ba. Amma babbar kyautar da nakeso nabaki daga zuciya ta itace kallon cikin idanuna dan ganin irin halittar da ubangiji ya maki. Gaskiya kina da kyau matuka. Inji turawa sukace “u look BEAUTIFUL”.

  42. Gaki kyakkyawa, ga far’a, ga mutunci, ga sanin kimar mutane, ga sanin yakamata, ga ilimi, ga bin iyaye, ga iya soyayya, iya rike masoyi, ni yanzu me ya rage mun? gaskiya kam babu, nasa mi abun da mutane ke muradi tattare da budurwa daya tak.

  43. Mai yuwa muna kusa da juna ko kuma nesa da juna, amma inaso kisaka azuciyar ki cewa ina sonki kuma babu abunda zai sana rabu dake, komin girman sa.

  44. Baby na, kinsan meyasa nake farin ciki? Dan nan ba da dadewa ba, zanga masoyiya ta abar kauna ta. Siyasa nake ta farin ciki kuma nakasa boyewa.

  45. Haryanzu nakasa yarda cewa rana daya dak ta wuce banji muryan ki ba, hakan yasa ni damuwa sosai, kuma hakan bazai kara faruwa ba kuma, nayi matukar kewarki sosai fiye da yadda kike tinani.

  46. Ni kyautar da nakeso a rayuwa itace kasan cewa tare dake walau cikin farin ciki ko bakin ciki. Inaso nazama silar farin ciki a rayuwar ki kamar yadda kika zamo tawa.

  47. Bakin cikina itace ba ko wani lokaci zamu rinka haduwa ba. Zan shiga damuwa sosai, amma kuma tinani ki zai yi maganin komai.

  48. Wasu lokutan daddare kowa na bacci amma banda ni, kinsan meyasa? Kyawun ki, tinani nake yadda rayuwa ta zai haskaka tare da kyakkyawar mace irin ki.

  49. Nasan bazaki yarda ba, amma wasu lokutan har manta yadda ake nunfashi nake duk inna kalli fuskar ki.

  50. Wani mawaki ya fadi cewa so yanada da wuya, idan ya shige ka baya fita, kuma naga alamar haka, don son ki ya shige ni ya hana sikuni, burina na faranta maki don ki kasance cikin farin ciki.

  51. Safiya tayi masoyiya, dafatan kin tashi cikin aminci da lafiyar jiki dana zuci? Har ila yau, ina mai kara mika godiya ta ga Ubangiji da yayi silar haduwa ta dake.

  52. Nayi tinanin zan iya yin shekara daya batare da ganin ki ba, amma hakan bazai yu ba tunda zuciya ta tashiga cikin wani hali dalilin rashin ganin ki na sa’a daya. Gaskiya nayi kewar ki sosai.

  53. Wasu mutanen in aka tambaye su menene dalilin farin cikinsu a duniya, kowa dai yana fadar tasa, amma da aka zo kaina bansan lokacin dana ambaci sunan ki ba.

  54. Nakan yi wasa akan wasu abubuwan amma yanzu nayi hankali na kara fahimtar fadan masana so cewa “mace kamar kwai take” haryanzu ina me kara gode maki na bani damar kasan cewa acikin zuciyar ki.

  55. Ana yawan tambaya ta menene sunan budurwar ka, amma sai n ace masu sunanta Baby, sai suce wannan ba suna bane, amsa ta itace banso kowa yagi sunan ki yagi yana son ki, dan kuwa zanyi kishi da hakan.

  56. Natashi da safiyar yau cikin farin ciki da walwala a dalilin samun budurwa irin ki, kinzama dalilin da ke sa zuciya ta farin ciki, me sani murmushi. 

  57. Kullin idanuna muradinsu, su gan ki, kunnuwa na kuma suji muryar ki, zuciya ta kuma tayi tinanin ki. Ina kaunar ki masoyiya ta.

  58. Duk inna zauna nikadai, sai nafara tinanin ki, tayaya nayi nasarar samun zuciyar ki,? Wannan shine tambayar da nake ma kaina a koda yaushe.

  59. Zaki ga wasu mazan suna cewa gida biyu maganin gobara, amma tunda na hadu da ke nagane cewa basu sami budurwa irin ki bane, dan duk saurayin da ya same ki, ba maganan gida biyu maganin gobara dan kuwa soyayyar ki zai sa yamanta cewa akwai wasu matan.

  60. yau nayi matukar sa’a dan muryar ki tasa nayi bacci cikin walwala da farin ciki, gashi kuma a safiyar yau, muryar ki ta bani dalilin farin ciki. Bansan wani irin hali zan shiga ba idan na rasa ki.

  61. Duk inna kalli wasu matan, sai nayi dariya a zuci, kinsan meyasa? Dan kyawun su bai kai akwantanta shi da taki ba. Ina muradin ganin ki.

  62. Ban taba gayama ki wannan sirrin ba. Amma yau zuciya ta ta saka zangayama ki, a duk sanda muke tare banso naga nadaina kallon ki, dan murmushin ki mai matukar kayatarwa ne tare da sa farin ciki acikin zuciya ta.

  63. Babban bakin cikina shi ne na wayi gari banji muryar ki ba, bansan wani hali kike ciki ba, gaskiya banyi wa kaina adalci ba idan har ban kyautata  maki ba, dan bazan iya biyan ki kwatankwancin hasken da kika zo dashi cikin rayuwa ta.

  64. Masoyiya ta inaso ki kalli cikin idanuna koda sau daya ne dan kiga irin soyayyar da zuciya ta take tafe da ita.

  65. Tin daga randa kika aminta da soyayya ta na fara ganin changi sosai, dan nadai na wasu abubuwa duk soboda dake, maganar gaskiya, duk saurayin da bai sami budurwa irin ki ba, baiyi dace ba.

  66. A duk sanda na zauna na natsu nake tinanin ki, karamin abu ke bata rai, dan banson komai na shiga tsakanina da ke.

  67. Wasu kanyi amfani da waya duk safiya suyi chatting, ko wani lamarin tasu, amma duk safiya inna dauki waya ta, abu na farko da nake yi shine na duba hoton ki, sa’an nan nakira ki, dan muryar ki abun son ji na ne.

  68. Na kasance banda hular sarauta, amma jina nake kamar sarki, koda ina cikin duhu babu fitilar haskawa, tinanin ki kawai yakan haskamun hanyar wucewa, na kasance banda karfin zuciya, amma soyayyar ki tayi maganin hakan.

  69. Idan na fada maki wata nasara da nasamu zakiyi mamakin jin hakan, abokaina harda wasu da bansani ba, sukan zo su tambayan, na basu shawarar yadda zasu tafiyar da soyayyar su cikin aminci kamar irin tawa. Kuma suna jindadin shawarar da nake basu

  70. Inada labari mai dadin da nake so na baki, amma kiyi mun alkawarin cewa sanda nake baki wannan labarin, zaki rinka kallon cikin idanuna ba kyapta ido. Dan ta hakan sakona zai iso zuwa wajen ki.

  71. Duk inna kira ki baki dauka ba sai na shiga damuwa, inna turo maki sako baki amsa ba, hakan nasami cikin damuwa fiye da yadda zan iya jure wa.

  72. Bayan nazari da tinani mai tsawo, nagane cewa kasancewar ki a rayuwa ta alkhairi ne, kuma zanso wannan alkhairin ya cigaba da wanzuwa har karshen rayuwa ta.

  73. Amma mai yasa duk lokaci in muna tare ban iya kallon cikin idanun ki, ina maki magana bakina na rawa, tare da rawan jiki, gaskiya kam kina da kwarjini matuka. Duk saurayin dake da budurwa irin ki bai da wata matsala, kuma ya rabauta.

  74. Ina sonki, nasha wannan kalmar ita ke nuna zahirin so, amma yanzu na fahimci me wannan kalmar ke nufi cikin sauki. Kuma wannan darasi da na koya bazai sulwanta ba.

  75. Gaskiya soyayya da mace mai ilimi, mai hankali, mai natsuwa, mai ladabi wacce tasan mutuncin mutane, babban rabo ce wanda bakowa ke iya samun hakan ba. Amma cikin sauki da tausasawa, nasami wannan rabon tare da mace daya. Gaskiya ni sarki ne.

  76. Kafin na same ki a rayuwa ta, na kasan ce mai wasa da komai, ban daukan abubuwa da mahimmanci, amma yanzu na waye, idanuna sun bude sosai duk a dalilin ki.

  77. Ina so naga fuskar ki a sanda kikayi kwalliya, naji muryar ki asanda kike cikin farin ciki, kalaman ki a sanda nake kallon cikin idanun ki, inna samu hakan, zan iya kyauta da duk abunda na mallaka dan soyayyar ki ta fiye mun komai. Farin cikin ki kawai ta ishe ni.

  78. Duk in kina tafiya tare da kawayen ki, sai nayi murmushi wanda har cikin zuci tattare take da nishadi, kinsan meyasa? Soboda acikin kawayen ki, ke tauraruwa ce mai haskaka samaniya, kyawun su bai bayyana a duk sanda kuke tare, dan ke sarauniyar kyawu ce.

  79. Nama kaina wani alkawari, kuma bazan taba bari wannan alkawarin ya sulwanta ba. Na ma kaina alkawarin faranta maki, cika maki duk burin ki matukar bai fi karfi na ba, zama dalilin murmushi da farin cikin ki. Muradi na ki kasan ce cikin farin ciki.

  80. Mace mai basira da tinani burin kowani namiji ce, shiyasa nakeso naga na mallake ki kizama tawa ni kadai. In kika zama tawa, burina yagama cika.

  81. Lokacin da muka sami sabani a tsakanin mu, nagane cewa bazan iya yin wuni daya ba tare da na san halin da kike cike ba. Na shiga wani yanayi da ankasa gane ni, me ke damuna, sai dai nace masu kar su damu, nina san meke damuna, bakomai bace face soyayyar ki. Nayi matukar kewar ki sosai.

  82. Bayan rabuwa ta da tsohuwar budurwa ta, tace mun intafi bazan taba sanin farin ciki, ko kwanciyar hankali ba, kamar yadda nasamu sanda muke tare, nace to ni ina maki fatan alkhairi, sai gashi yau nasami farin ciki da kwanciyar hankali fiye da yadda nasamu sanda muke tare duk adalilin ki.

  83. Nasamu labarin mutane nasan su shiga tsakanin mu su raba mu dan suna bakin ciki da irin soyayyar da ke tsakanin mu wanda basu same ta ba. Ina so kisan cewa hakan bazai faru ba, dan bazan yi kasa a gwiwa ba dan ganin nasami karbuwa a zuciyar ki.

  84. Abokina yace mun wai yanasan budurwar sa sosai soboda tana bashi nishadi, a farko banso na tinka mai ba, amma da maganan sa yayi yawa, sai na tambaye shi, wani irin nishadi take baka? yana gama fada mun na fashe da dariya, in aka auna a mizani, nishadin da nake samu a wurin ki da wanda yake samu a wurin ta, nashi bazai fito ba kwata kwata.

  85. Ban iya waka ba amma a dalilin ki naje na koyo waka, dan saki dariya da kuma kara damkon soyayya a tsakanin mu.

  86. Zuciya ta ta aiko ni da wata sako mai wuyan fada, bansan ya zaki ji sa ba, amma dai, ina kaunar ki.

  87. Inaso kifada mun wani abu guda biyu, kuma, bazan yi kasa a gwiwa ba gurin aikata su. Na farko abun da kike so nayi wanda zai faranta maki rai da kuma wanda inna kiyaye su zamu zauna lafiya.

  88. Masana so su kan fadi cewa soyayya ruwan zuma ce, amma nidai anawa fahimtar na dauki so a matsayin zanen kaddara.

  89. Meyasa nake yawan kewar ki haka ne, gaskiya ban tinanin zan iya rayuwa ba tare da ganin fuskar ki ba.

  90. Akace garin masoya baya nesa, amma kuma bansan meyasa nake yawan kewar ki a cikin kwana kin nan ba. 

  91. Amma kinsan irin kyawun da kike dashi? In ina jin yunwa ko cikin damuwa, tinanin ki kawai yakan kosar dani, in ina kallar hoton ki, nakan ji karfi a cikin zuciya ta.

  92. Ga sako daga zuciya ta zuwa gare ki, ina matukar kaunar ki.

  93. Bansan meyasa soyayyar ki karuwa take a zuciya ta ba kullin? Wannan shi ake kira da so ta gaskiya.

  94. Nakan danyi wasa wasu lokutan, amma fa duk abunda na fada maki game da soyayyar mu da gaske nakeyi babu wasa acikin ta.

  95. Yan mata adan gari, farin cikin rayuwa ta, sarauniyar a zuciya ta, kyawunki na haska samaniya, duk inda kika bi sai ansan da zuwan ki badan ganin ki ba kawai amma harda farin jinin ki.

  96. Ranar da kika amsa kina sona bayan na koma gida bansan lokacin da hawayen farin ciki ya fara zuban mun ba, ni kaina nayi mama kin hakan sosai. Soyayyar ki ce tazo da hakan.

  97. Bayan na zauna yau da safiya na roki Ubangiji ya hadani da alkhairin yau, kawai sai naga kiran ki, hakan shine alkhairin dana fara gani bayan na fita daga gida.

  98. Tun ran da nafara ganin ki zuciya ta ta daina samun sukuni. Kin shiga zuciya ta kin hana kowa shigar ta.

  99. Duk inna yi wanka zanzo gidan ku, sai nai ta kishi soboda nasan duk irin wankan danayi, sai kinfi ni kyau.

  100. Kalmar ina son ki na dauke da jumla uku, soboda haka, a rana irin ta yau nayi maki alkawari guda uku. Na farko, zama dalilin farin cikin ki, na biyu, cika maki duk burin ki matukar bai fi karfi na ba, na karshe kuma, barin duk abunda zai saki cikin damuwa.

  101. Masoyiya ta, kowani da’ namiji na da burin da yake so yaga ya cika a rayuwar sa. Ni wannan buri nawa ita ce na kyautata maki har karshen rayuwa ta. Kasancewar ki cikin farin ciki shine alkawarin da na daukan ma kaina.

  102. Kullin zuciya ta ke kadai take son gani acikin ta. Bata samun kwanciyar hankali inbata ganki ba. Wasu lokutan sai naba ta hakuri nace mata kina nan ba kin fita daga cikin ta bane. Ina son ki!

  103. Kinsa na kasance cikin farin ciki wanda ban taba shiga irin ta ba, na daina shiga cikin damuwa kamar yadda nake shiga a baya. A duk sanda na shiga damuwa, sai tinanin ki yazomun; shikenan karshen damuwan.

  104. Sarauniya ta, soyayyarki ta kawo mun duk wani nishadi da nake so a rayuwa ta. Ke ta musamman ce a cikin mata. Samun budurwa kamar ki kamar samo allura ne a cikin teku, kuma nashiga naso ki. Farin cikin danake ciki, ke ce sila.

  105. Masoyiya ta abar kauna ta, nadade ina neman budurwa wacce zuciyar ta ke cike da soyayya, sai gashi kaddara ta hadani dake alokacin danake bukatar ki. Nagode da kasancewa cikin rayuwa ta.

  106. Bara nabaki wata labari mai dadi; wata rana ana cikin bani labarin wasu masoya biyu masu kaunar junan su sosai nasaka araina wannan labarin sai ta zama tawa. Kuma gashi yau nazama wannan masoyin mai son sarauniyar sa kuma kinzama wannan masoyiyar me kula da masoyin ta.

  107. Bansan meyasa bana so kina nesa dani ba. Aduk sanda baki kusa dani, ji nake kamar an raba ni da abu mafi soyuwa acikin zuciya ta. Daso samune, da angwar ku zanzo na tare soboda na rinka ganin ki kullin dan na samu kwanciyar hankali, zuciya ta kuma tasamu natsuwa.

  108. Kamar yadda nasami zuciyar ki batare da nayi takara ba, batare da ni jinin sarauta ba, zanyi duk abunda zai sa zama na a cikin wannan zuciya tazamo abun misaltawa a tsakanin wasu masoyan.

  109. So kawai na nema a wurin ki, amma kin bani so da farin ciki. Wannan kyautar da kika mun ba abunda zan iya sulwantar wa bane. Ya shiga cikin tarihin rayuwa ta. 

  110. Na kira ki masoyiya ta dan kin shigo cikin rayuwa ta tare da so, da farin ciki. Na kira ki sarauniya dan kece ke rike da makullin zuciya ta. Na kira ki abar kauna ta dan duk wani nishadin dake rayuwa ta, ke ce silar ta.

  111. Na bukaci fure, amma kinbani gaba daya gonar ta. Na bukaci dugon so, amma kin shayar dani tekun ta. Na bukaci rayuwa, amma kinbani dalilin rayuwa. Na bukaci masoyiya, amma sai nasani kyautar aminiya. Inason ki.

  112. Kinzamo babbar kyauta wanda bantaba samun irin ta ba a rayuwa ta. Kece irin macen da duk wani namiji ke mafarkin samu a rayuwar sa.

  113. Masoyiya ta abar kauna ta, dafatan kintashi lafiya, na turo maki wannan sakon ne badan komai ba sai dan na tina maki akwai wani saurayi na nan yana tinanin ki, yana farin cikin samun ki a rayuwar sa.

  114. In aka tamabaye ni na misalta irin soyayyar da nake maki, sai nace kamar yawan ruwan dake cikin kogi, kamar adadin furen dake daji, kamar adadin jijiyar dake jikin mutum. Gaskiya kin wuce hakan a cikin zuciya ta.

  115. Wasu ranakun sai naji ina sonki fiye da komai wasu ranakun kuma bahaka bane, amma fa inaso kisani cewa babu wata rana guda daya da zai wuce banyi kewar ki ba. Zuciya ta nasan ganin ki a kusa da ita.

  116. Wasu lokutan ina da ayyuka masu yawa akaina, amma daga sanda tinaninki yazomun sai dai komai ya fitan mun a rai. Ayyukan su koma basu da mahimmanci soboda tinanin abar kaunata.

  117. Aduk sanda kike cikin damuwa ko kingaji, ga kafada ta ki dafa, ga kirgina ki kwanta akai matukar hakan zai kawo maki natsuwa. Ina son ki sosai. 

  118. Nafada maki wani abu abar kauna ta? Bazan taba baki zuciya ta ba. Dan wannan zuciyar ta riga ta kasance taki ce. Nabaki kyautar ta.

  119. Aduk sanda kike tare da wasu matan ko kawayen ki, sai kizama kamar tauraruwa ta musamman a cikin wasu taurarin, kizamo kamar jar fure mai kyawun gaske a cikin gonar ta. Duk namiji mai cewa gida biyu maganin gobara to bai samu kamar ki bane.

  120. Ya zaki ji a zuciyar ki a sanda kika tashi daga bacci tare dani a kusa dake yayin da nake kallon cikin idanun ki masu kyau. Irin wannan lokacin ba bun da za’a manta bane.

  121. Sannu da wannan lokaci masoyiya, nasan yanzu kina jin bacci kuma banso nazo na dameki dan haka, sanda kike bacci, zanzo maki acikin mafarki dan na nuna maki yadda nake son ki, kullin kina cikin tinani na.

  122. Zuciya ta na kasancewa cikin damuwa a sanda baki kusa da ita. har tasa nafara tinanin yadda rayuwa ta zata kasance batare da ke a cikin ta ba. Wannan rayuwar ba abun nema bane dan cike take da bakin ciki. Kiyi hakuri kisance a cikin rayuwa ta.

  123. Bakisan abunda ya faru ba jiya daddare, na zauna nafara tinanin menene a salin dalilin da yasa nafara sonki, abun mamakin shine tin jiya nake rubuta wannan dalilan amma gashi safiya tayi amma ko rabin abun da zan rubuta ban riga na rubuta ba.

  124. Farin cikin ki shine farin ciki na, damuwar ki damuwa ta ce dan banga amfanin kasancewa cikin farin ki ba masoyiya ta na cikin damuwa. Inaso kiyi mun wani alkawari guda daya, a duk sanda kike cikin damuwa ki sanar dani.

  125. Wasu lokutan sai azo ace mun kinyi kaza da kaza dan naji haushin ki, amma kuma abun mamakin anan shine a sanda suke cemun hakan sai naji kamar a ranan ne nafara son ki. Soyayyar ki ya gama maimaye ni.

  126. Kiyi hakuri masoyiya ta, abaya, na kasance ina yin abubuwa wanda baki so, masu bata maki rai amma nakasa fahimtar hakan, amma yanzu nagane kuskure na, soboda hakan ne ke baki hakuri akan duk wani hali da kika shiga soboda ni. Zuciya ta tana kewar ki.

  127. Babu fatar da nake maki a rayuwa face kasancewa cikin nasara, dacewa a cikin duk lamarin ki na yau da kullin. 

  128. Zan zama babban makaryaci idan nace maki ban kewar ki. haka karya ce. Ni yanzu muryar ki kawai nake son ji a yanzu haka.

  129. Wani mawaki a wakar sa yace ”ke nake gani, in banda ke, bazan kula kowa ba” kuma wannan gaskiya ce dari bisa dari. Muradina shine ki kasance akusa dani idanuna su ganki, zuciya ta taji dadi, kunni na suji muryar ki. Hakan ya ishe ni komai.

  130. Ina matukar jindadin yadda kike kallo na inmuka hadu. Yadda kike murmushi, yadda kike taka sahon ki kina kallon cikin idanuna da murmushin ki mai makutar kayatar wa. Hakan na bani nishadi sosai.

  131. Ba yau muka hadu dake ba, amma duk inna kalli fuskar ki a sanda kike murmushi, sai naga murmushin ki na burge ni kamar yau nafara ganin ki kina yi. Duk mai neman maganin damuwa, yasa mu budurwa irin ki yagama shiga damuwa.

  132. Duk inna ce maki ina son ki, ina nufin ina sonki ne da gaba daya zuciya ta kuma fiye da yadda kike sona. A shirye nake na fuskanci duk wani kalubane dake tattare da rayuwar mu tare.

  133. Kinsan meyasa nake cikin farin ciki, dan nasami duk wani dalilin da zai zamo silar farin ciki da natsuwa soboda ke sarauniya ta.

  134. Ga wata addu’ar da zan mana, ubangiji yasa wannan haduwar tamu tazama haduwar da daya da daya zai koma 2, 3, 4, 5, 6, 7 ko mafificin hakan dan kuwa inaso na kare rayuwa ta dake a cikin ta.

  135. Yanzu nasan dalilin da yasa nakasa barin wannan gari mai albarka, ashe wacce zata zama silar farin ciki na boye a cikin wannan garin. Gaskiya wannan gari yayi mun taimako kuma bazan taba mantawa da wannan taimakon ba.

  136. Duk wanda yazo ya tambaye ni me ake nufi da so ta gaskiya kinsan mene zan nuna masa? Hoton ki zan dauko na nuna masa dan gane ya so ta gaskiya take. Wannan ba zake wa bace, al’amarin gaskiya ce. 

  137. Kyawunki karuwa yake a duk sanda nakara kallon fuskar ki, hakan ne yasa kallon fuskar ki tazama muradina na farko.

  138. Bantaba yin dana sanin samunki ba kuma bazanyi yau ba, ba gobe ba, ba za’ayi hakan ba. Kin riga kin samar wa rayuwa ta maganin matsalar ta.

  139. Bantaba tinanin zan zama abunda nazama ba sai da kaddara ta hadani dani dake lokacin da nayi tinanin na rasa komai. Da zaki fahimci me nake shiga aduk sanda nake tinanin ki, da zaki san meyasa nake kusa dake a koda yaushe.

  140. Bansan me ake nufi da nasara ba sai dana same ki, inban da nasara babu abunda nasamu daga gareki. Damuwa da bakin ciki sun gudu, farin ciki da natsuwa yasamu wurin zama. Nagode sosai da wannan kula da kike nuna mun. kifada mun abunda kike so na maki.

  141. Masoyiya ta, tinanin ki ke zama abunda nafi yi a kullin, duk safiya bayan na tashi da kuma dare a sanda zan kwanta, wasu lokutan har farkawa nakeyi cikin dare naita tinanin ki.

  142. Mace daya tak a cikin dubu,yar budurwa ta abun muradi na. kinzamo mafi kusanci a cikin zuciya ta. Bugawar zuciya ta da tinanin ki tare suke tafiya.

  143. Duk inda kika je, ina tare da ke, walau muna tare ko kuma acikin zuciyar ki. Babu abun da zai taba rabamu da ke. Nasara tamu ce.

  144. Koda ace zamuyi shekara goma bamu hadu ba, soyayyar ki a cikin zuciya ta bazata taba raguwa ba sai dai ma ya karu a cikin ta.

  145. A duk sanda nake cikin wani damuwa, babu abunda zuciya ta take so a wannan lokacin sai ke. Ke suke son gani, muryar ki suke son ji, zahirin ki suke muradi.

  146. Kinsan mene ke bani mamaki gama da soyayyar mu, wasu lokutan muna tare da juna, wasu lokutan muyi fada tsakaninmu, wasu lokutan ma har daina wa juna magana mukeyi, amma hakan baisa soyayyar mu tasami matsala ba.

  147. Kasancewa ta a cikin tinanin ki nasani kokwanto a kan son da kike nuna mun. Amma banda kokwanto akan kasancewa ta acikin zuciyar ki, shiyasa a kullin nake son kara fatar kasancewa acikin ta ni kadai .

  148. Zan iya rubuta wakoki bila adadin dan yabar kyawun ki, amma duk da hakan hankali na bazai kwanta ba soboda duk abunda na rubuta acikin wakan, bai isa a misalta shi dake ba. Budurwa ta ta daban ce a cikin yammata.

  149. Babbar farin ciki na shine na tashi duk safiya da tinanin akwai wacce ta damu dani. Idan aka tambaye ni na lissafa abubuwan danayi nasarar samu, soyayyar ki na cikin wadandan nasaran dana samu. Manta ki abu ne wanda bazai taba faruwa ba.

  150. Ance dani na misalta soyayyar dake tsakanin mu. Sai nace dasu, kamar yadda mayen karfe bazasu taba rabuwa da juna ba matukar suna tare, haka ni da ke babu abunda zai iya raba mu da juna.

  151. Koda da wasa, banaso nayi tinanin rana daya batare da nagan ki ba. Babu wani sa’a da zata wuce daga cikin rayuwa ta banyi tinanin abar kauna ta ba. Inaso kizama tawa nazama naki.

  152. Zuciya ta na da wani mabudi wanda babu wanda yasan da ita. wannan mabudin ba kowa bace sai ke, duk mai son shiga zuciya ta sai yayi dan kuwa akwai mai ita.

  153. Aduk sanda nake cikin damuwa ko bakin ciki, babu abunda nake muradin gani a wannan lokacin sai ke masoyiya ta. Duk inna ganki naga farin ciki.

  154. Kina da matukar kyau. Wasu lokutan har tambayan kaina nake akan ina kika samo wannan kyau haka amma ban samun gamsasshiyar amsa, samun irin ki ba wasan da yaro zai fara bane.

  155. Inaso na fada maki cewa duk inda nake, a duk halin da nake ciki, ina tinanin ki, tinanin lokuta da mukayi na jindadi. Mu ajiye labarin soyayyar mu tarihi dan muba yaran mu nan gaba.

  156. Na san bazaki fahimci sirrin da ke cikin murmushin ki ba. Amma duk damuwar da saurayi zai shiga ko wani rashin natsuwa, daga sanda yayi ido biyu da ke kuma shikenan karshen damuwan, daga nan kuma ma sai farin ciki.

  157. Duk wani abun da muka riga da mukayi a baya na cikin kaina dan na ringa tinawa dake. Bakin ciki bazai iya zuwa kusa da inda nake ba. 

  158. Kafin na hadu da ke a rayuwa ta, na dade ina mafarkin wata sarauniya wanda nakasa gane wacece, amma dai abunda bazan manta ba shine farin ciki da take sani. Amma tunda nahadu dake na tabbatar cewa ke ce wannan sarauniyan danake gani acikin bacci na. yanzu na yarda da cewa wasu mafarkin na zamowa zahiri.

  159. Masana lafiya sunce kallon shuka na kara lafiyar idanu, amma ni kallon cikin idanun ki sunfi kara mun lafiya fiye da kallon cikin shuka. Nasan bazaki fahimci hakan ba.

  160. Ina son ki, so wanda bantaba wa kowa ba. Ina kaunar ki, irin kaunar da bantaba wa kowa ba. Ina kewar ki, irin kewar da banta ba wa kowa ba. Ina so na kasance tare da ke, irin kasancewa da bantaba yi da kowa ba, inaso na zauna tare dake, irin zaman da bantaba yi da kowa ba.

  161. Kinyi mun wasu abubuwa dayawa da dama, amma babu abunda namaki sai son ki da zuciya ta. Kina da amfani sosai a rayuwa ta, farin cikin ki ita ce abun da nake muradin gani.

  162. Inda yanzu zan tsaga maki zuciya ta kigani, babu abunda zaki gani acikin ta face so na gaskiya da kuma farin ciki. Nima hakan nakeso ki kasance. Ban san ta ina zan fara fada maki yadda nake son ki ba.

  163. Kinsan wani abun mamaki, duk inna fita na kalli wata mace a waje bake ba, sai zuciya ta tafara fushi dani, idanuna su fara fushi dani, ba karamar wahala nake sha wurin shawo kansu ba.

  164. Ke ce macen dana dade ina nema dan zuciya ta ta cika, kuma gashi nasa meki a sa’a. yanzu kam nazama cikakken namiji. Shigowar ki rayuwa ta babu abunda bata chanza ba a tare dani.

  165. A duk sanda nace ma zuciya ta zanyi gasa da ita akan ki, sai tace mun kanaso kayi gasa da wacce ta zamo tana ciki na, wacce farin cikin ta ke bani karfi. sai anan nagane cewa zuciya ta taki ce.

  166. Wasu lokutan zaki ga ina wasu abubuwan kamar bandamu da ke ba. Inaso ki sani acikin zuciya ta, ke ce ta farko. Umarnin ki ce umarnin da zuciya ta ke bi a kullin.

  167. Kalmar so tana dauke da harfa biyu kachal. Amma a zahiri in aka ce so, tinanin ki ke zuwan mun. ina son ki.

  168. Ina kewar sarauniya ta akusa dani, na kwanta amma nakasa bacci. Jinake kamar daren na kara tsawaita. Nakosa gari ya waye, soboda naji muryar masoyiya ta. Kuma nakara kallon cikin idanun ta nace ina son ki.

  169. Duk inna tina sunbatar da kika yi mun duk safiya, sai su zama mafarin farin ciki da samar da natsuwa a zuciya ta.

  170. Wasu matan kyawun su ya wuce misaltawa, kuma anan na samo ki cikin wadandan kyawawan halittan. Kuma duk wani abu da zai sa wannan kyawun ya cigaba da kasance wa, shine muradina.

  171. Nasan zakiyi mamaki duk inna ce maki banjin yunwa aduk sanda muke tare, kallon fuskar ki kawai na kaudar mun da yunwa koda ace nayi wuni daya banci abinci ba.

  172. Bantaba ganin budurwa wacce zuciyar ta ke cike da farin ciki kamar ke ba. Bantaba ganin budurwa wacce tasan sirrin share damuwa daga zuciyar saurayi kamar ki ba. Nayi dacen samun ki a rayuwa ta.

  173. Ina son ki soboda dalilai dayawa, amma asalin dalilin daya sa nake kaunar ki, nake so na kasance tare dake har karshen rayuwa ta ita ce kyakkyawar zuciyan da kike da ita. Shi kadai ta ishe ni farin ciki.

  174. Acikin wannan duniyar da muke ciki, bantaba tinanin zan taba son wata budurwa kamar yadda nake son ki ba koda me zai faru a tsakanin mu. Zuciyar ki ce ta dace da zama na.

  175. Kafin nasanki ni ragone, banda wata buri a rayuwa ta, amma gashi daga samun ki har nasamu burika dayawa da nake so na cika su. Daya daga cikin su shine kyautata maki har karshen rayuwa ta.

  176. Duk dariyan da zanyi a kullin, kece dalili, duk farin cikin da zan shiga a kulkin, ke ce sila, duk wani natsuwa da zan shiga a kowacce rana, murmushin ki ce silar hakan. Bazan taba mantawa da wannan soyayyar dake tsakanin mu ba.

  177. Wasu dai sunce so nada iyakar ta, amma fa nibanga wannan iya kar ba, dan kuwa kullin kara son ki nake, kara kusan tar ki nake, buri kan mu cika suke. Nazama daya daga cikin maza masu sa’a a duniyar nan.

  178. Indai kasa a ranka soyayya tana da iyaka, to bazaka taba jindadin soyayyar kaba, dan haka ni da ke “muta ka raba” nidake zamuyi rayuwa tare mu kafa tarihin da zamu zama abun koyi.

  179. Duk sa’ar da ta wuce banganki ba, ji nake kamar munyi shekaru bamu hadu da juna ba. Kizo ki kawo mun agaji. Zuciya ta bataso tana kewar ki. Ina so kiyi mun wata alkawari guda daya; bazaki yi nesa dani ba.

  180. Yanzu dai ga zuciya ta nabaki kyauta. Duk abunda zaki sa acikin ta kisa, duk yadda zaki yi da ita kiyi. Tazama taki ke kadai.

  181. A kullin ina ganin mata daban daban amma duk da haka bansamu wacce ta kwanta mun a rai ba. Amma daga kallo daya kika sace zuciya ta, daga wannan ranar na kasa samun sukuni shiyasa nazo na sanar maki da sakon da zuciya ta ke dauke da ita. ina son ki!

  182. Ance dani idan kana cikin wani hali, daga sanda ka fada ma wani abunda ke damun ka, kamar kasami amsar ne. amma abun mamakin shine a duk sanda nake cikin damuwa kina sani ba tare da na fada maki ba duk da ina boye maki. Nagode sosai da wannan kulawa da kike nuna mun.

  183. Bantaba haduwa da wata wacce take nufi na da alkhairi da so na asali kamar ki ba. Ga mutun tawa, ga kulawa, ga sanin kimar mutane. Ni yanzu jinake kamar nasami matar da zan aura mu zauna tare cikin aminci.

  184. Ance soyayya ba’a ganin ta, sai dai ajita a zuciya, amma daga haduwar mu dake na karyata wannan maganar, dan inna kalli cikin idanun ki babu abinda nake gani face so na gaskiya.

  185. Macen da zata soni kawai na nema, amma nasami wacce take so na da zuciyar ta, take kulawa dani fiye da yadda na kula da kaina abaya, mai share mun duk wani damuwa na da bakin ciki. Wannan ranar da nake mafarki ya kusa zuwa.

  186. Na kasance namiji mai tsoro da kuma far gaba, amma ganin zan iya rasaki ya sa wannan tsoron danake fama da ita ta barni duk a dalilin ki, wannan ma kawai abun godiya ce, dan bakowa yasa mi irin ta ba. Yanzu dai zan iya kallon cikin idanun ki nafada maki abun da zuciya ta ke dauke da ita.

  187. Akace mun akwai aljanna a duniya, nace karyane, amma wannan soyayya da kika shayar dani da ita, tasa yanzu na gasgata hakan. Soyayya ruwan zuma.

  188. Duk in muna tare sai naga kamar kinfi kyau a zahiri fiye da yadda kike a hoto, in kuma ina gida ina kallar hoton ki, sai kuma naga kinfi kyau a hoto fiye da yadda kike a zahiri. Yabaki dariya koh? Amma meyasa tinani na ke raya mun hakan.

  189. A duk sanda naje siyar kati inzan kiraki a waya, sai naji farin cikin wacce bantaba jin irin taba, alokacin da kuma mukafara waya kuma, sai naji kamar kada katin yakare. Muryar kina kara wa kunnuwa na lapiya.

  190. Nafada maki wani abu? Daga sanda dare tayi, in banda tinanin ki babu wani abun da nakeyi har gari ya waye, hakan ne yasa duk safiya inna tashi nake kokarin kiran wayan ki dan nasani halin da kike ciki. Dafatan kina lafiya.

  191. Akwai abunda har yanzu inna fada gani ake kamar ina sunbatu, duk safiya inna tashi daga bacci na bude idanuna ke ce nake fara gani. Amma kowa na ganin kamar wasa nakeyi. Kina zuciya ta a koda yaushe.

  192. Zai iya yuwa kina sona ko kuma baki sona, amma inaso kisani kina cikin zuciya ta kuma ba abunda zai sa soyayyar danake maki ta gushe.

  193. Inaso na boye ki a cikin zuciya ta na kulle. Acikin zuciya ta sai kiyi mulkin ki a matsayin ki sarauniya, yadda babu wanda zai iya ganin ki. Dan haka nabaki kyautar zuciya ta.

  194. Daga sanda na wayi gari banji muryar ki ba ko banki ba, sai naji na fara kewar ki kamar munyi shekaru bamu hadu da juna ba. Inda da hali, zan iya tare wa a angwar ku dan na fito duk safiya soboda ke.

  195. Kalamai sun kare a baki na, banda wani kalma data rage a zuciya ta sai wasu kalmomi uku wacce kin sansu, INA SON KI!

  196. Duba ga yanayin yadda kika soni da kuma irin kulawar da kike nun mun. na riga nayi shawara da zuciya ta, kuma suna maraba da zuwan ki cikin ta. Duk wata natsuwa da suke samu duk soboda ke ce.

  197. Masoyiya ta, inaso mu fita cikin gari muje inda babu surutu, sai dai tsuntsaye masu rera waka, shukoki wasu bamu iskar da muke shaka, musha soyayar mu ba tare da wata waswasi ba. Dan ina so ki manta da duk damuwar ki.

  198. Bana bukatar na fada maki irin kaunar da nake maki abar kauna ta, dan amsar tambayan; kina cikin idanuna, ki kalli fuska ta, zaki ga hakan.

  199. Kina cikin zuciya ta, kinsan ya akayi nagane hakan, dan duk bugawan zuciya ta, sunan ki take kira masoyiya ta.

  200. Na kasance ina wasu abubuwa da ban fada maki suba dan cin ma wata buri da manufa, wannan manufar bata komai bace illa kyautata maki har karshen rayuwa ta.



Comments

Post a Comment

Drop Comment here

Popular posts from this blog

1000+ Kalaman Soyayya Masu Dadi Da Ratsa Zuciya Harda Nishadantarwa 2023

180+ Sakonnin Soyayya SMS na Safe, Rana, da Dare [Masoya Maza da Mata]

Kalaman Yabon Budurwa